Shugaban ƙasar Ghana John Dramani Mahamaya ya jagoranci shiru na girmamawa a fadar gwamnatin ƙasa ta Jubilee House kafin a rantsar da sabbin alƙalai 37 da aka naɗa a manyan kotun ƙasar.
Shugaban ya tabbatar da cewa an sanar da gwamnatin rasuwarta a hukumance kuma a jawabinsa ga jami’ai na fannin shari’a da ‘yan siyasa ya nemi a haɗa kai a girmama matar da zama ‘yar takarar shugaban ƙasa a shekarar 2016.
Tsohon shugaban ƙasa Nana Addo Dankwa Akufo-Addo, ya fitar da wata sanarwa inda ya bayyana alhininsa game da rasuwar Nana Konadu Agyeman-Rawlings, yana mai bayyana ta a matsayin “mata mai ƙarfin yarda da sha’awar ƙarfafa wa matan Ghana gwiwa.”
Gidan rediyon Joy FM na ƙasar ya ruwaito cewa ɗaukacin ‘yan Ghana — mata ‘yan kasuwa da manoma da malamai a karkara — sun ji zafin rasuwarta sosai. Suna ganin kansu cikin jajircewar matar da, duk da cewa ta bar fadar shugaban ƙasa, ta ci gaba da takara.
Ta yi wa’adi biyu a matsayin matar shugaban ƙasa — ta yi wani gajeren wa’adi a shekarar 1979 da kuma dogon wa’adi daga shekarar 1981 zuwa shekarar 2001 — inda ta sake fasalin kujerar daga mai uwargida ta zamantakewa kawai zuwa wani muƙami mai ƙarfi da ke tasiri kan siyasa.